Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mak 1:12-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

12. “Dukanku masu wucewa, ba wani abu ba ne a gare ku?Ku duba, ku gani, ko akwai baƙin ciki irin nawa,Wanda Ubangiji ya ɗora mini,A ranar fushinsa mai zafi.

13. “Daga sama ya aukar da wuta a cikin ƙasusuwana.Ya kuma kafa wa ƙafafuna ashibta,Ya komar da ni baya,Ya bar ni a yashe, sumamme dukan yini.

14. “Ubangiji ya tattara laifofinaYa yi karkiya da su,Ya ɗaura su a wuyana,Ya sa ƙarfina ya kāsa.Ya kuma bashe ni a hannunWaɗanda ban iya kome da su ba.

15. “Ubangiji ya yi watsi da majiya ƙarfina,Ya kirawo taron jama'a a kainaDon su murƙushe samarina.Ya kuma tattake Urushalima, zaɓaɓɓiyarsa,Kamar 'ya'yan inabi a wurin matsewa.

16. “Ina kuka saboda waɗannan abubuwa,Hawaye suna zuba sharaf-sharaf daga idanuna.Gama mai ta'azantar da ni,Wanda zai sa in murmure yana nesa da ni.'Ya'yana sun lalace,Gama maƙiyi ya yi nasara!”

17. Sihiyona tana miƙa hannuwanta,Amma ba wanda zai ta'azantar da ita.Gama Ubangiji ya umarci maƙwabtan Yakubu su zama maƙiyansa.Urushalima kuma ta zama ƙazantacciya a tsakaninsu.

18. “Abin da Ubangiji ya yi daidai ne,Gama ni na ƙi bin maganarsa,Ku ji, ya ku jama'a duka,Ku dubi wahalata,'Yan matana da samarina,An kai su bauta!

19. “Na kira masoyana, amma suka yaudare ni,Firistocina da dattawana a cikin birni sun hallakaSaboda neman abincin da za su ci su rayu.

20. “Ka duba, ya Ubangiji, ina shan wahala,Raina yana cikin damuwa,Zuciyata tana makyarkyata saboda tayarwata.A titi takobi yana karkashewa,A gida kuma ga mutuwa.

21. “Sun ji yadda nake nishi,Ba mai ta'azantar da ni.Dukan maƙiyana sun ji labarin wahalar da nake ciki,Suna kuwa murna da ka yi haka.Ka kawo ranan nan da ka ambata,Domin su ma su zama kamar yadda nake.

Karanta cikakken babi Mak 1