Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

M. Sh 33:18-22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

18. A kan Zabaluna ya ce,“Ka yi murna da tafiye-tafiyenka, ya Zabaluna,Kai kuma Issaka, cikin alfarwanka.

19. Za su kira mutane zuwa dutse,Can za su miƙa hadayu masu dacewa,Gama za su ɗebo wadatar tekuna,Da ɓoyayyun dukiyar yashi.”

20. A kan Gad, ya ce,“Mai albarka ne wanda ya fāɗaɗa Gad,Gad yana sanɗa kamar zaki,Yana yayyage hannu da ƙoƙon kai.

21. Zai zaɓar wa kansa wuri mai kyau,Gama wurin ne aka keɓe wa shugaba.Ya zo wurin shugabannin mutane,Tare da Isra'ila, ya aikata adalcin Ubangiji,Ya kiyaye farillansa.”

22. A kan Dan, ya ce,“Dan ɗan zaki ne,Mai tsalle daga Bashan.”

Karanta cikakken babi M. Sh 33