Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

M. Sh 32:32-50 Littafi Mai Tsarki (HAU)

32. Kurangar inabinsu daga kurangar inabin Saduma neDa gonakin Gwamrata.'Ya'yan inabinsu dafi ne,Nonnansu masu ɗaci ne.

33. Ruwan inabinsu dafin macizai ne.Da mugun dafin kumurci.

34. “ ‘Wannan ba a jibge suke a rumbunana ba,A ƙulle kuma a taskokina?

35. Sakayya da ɗaukar fansa nawa ne,A lokacin ƙafarsu za ta zame,Gama ranar masifarsu ta kusa,Hallakarsu za ta zo da sauri.’

36. Ubangiji zai ɗauka wa jama'arsa fansa,Zai ji ƙan bayinsa,Sa'ad da ya ga ƙarfinsu ya kāsa,Ba kuma wanda ya ragu, bawa ko ɗa.

37. Sa'an nan zai ce, ‘Ina gumakansu,Dutse wanda suka nemi mafaka gare shi,

38. Waɗanda suka ci kitsen hadayunsu,Suka sha ruwan inabin hadayarsu ta sha?Bari su tashi su taimake ku,Bari su zama mafaka!

39. “ ‘Ku duba fa, ni ne shi,Ba wani Allah, banda ni,Nakan kashe, in rayar,Nakan sa rauni, nakan kuma warkar,Ba wanda zai cece su daga hannuna.

40. Na ɗaga hannuna sama,Na rantse da madawwamin raina,

41. Sa'ad da na wasa takobina mai walƙiya,Na riƙe shi da hannuna don yin hukunci,Zan ɗauki fansa a kan magabtanaZan sāka wa maƙiyana.

42. Zan sa kibauna su bugu da jini,Takobina zai ci nama,Da jinin kisassu da na kamammu,Da ƙoƙon kan shugabannin maƙiya.’

43. “Ya ku al'ummai, ku yabi jama'arsa,Gama zai rama wa bayinsa saboda jininsu,Zai ɗauki fansa a kan magabtansa,Zai tsarkake ƙasar jama'arsa.”

44. Sai Musa da Joshuwa ɗan Nun suka zo, suka hurta dukan kalmomin wannan waƙa a kunnen jama'a.

45. Sa'ad da Musa ya gama hurta waɗannan kalmomi ga Isra'ila,

46. ya ce musu, “Ku riƙe dukan waɗannan kalmomi a zuciyarku, waɗanda nake yi muku kashedi da su a yau don ku umarci 'ya'yanku su kiyaye dukan maganar dokokin nan sosai.

47. Wannan ba magana kurum ba ce, amma ranku ne. Ta wurin wannan magana ce za ku yi tsawon rai a ƙasar da za ku haye Urdun zuwa ciki don ku mallake ta.”

48. A wannan rana ce Ubangiji ya ce wa Musa,

49. “Ka hau duwatsun Abarim, wato Dutsen Nebo wanda yake a ƙasar Mowab, daura da Yariko, ka duba ƙasar Kan'ana wadda zan ba Isra'ilawa su mallaka.

50. Za ka rasu a kan dutsen da za ka hau, za a kai ka wurin mutanen da suka riga ka gidan gaskiya, kamar yadda ɗan'uwanka, Haruna, ya rasu a Dutsen Hor, aka kai shi wurin mutanensa waɗanda suka riga shi gidan gaskiya.

Karanta cikakken babi M. Sh 32