Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

M. Sh 15:4-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

4. “Ba za a sami matalauci a cikinku ba, da yake Ubangiji Allahnku zai sa muku albarka a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ita gādo, ku mallaka,

5. muddin kun yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnku, kuna kiyaye wannan umarni da na umarce ku da shi yau.

6. Ubangiji Allahnku zai sa muku albarka kamar yadda ya alkawarta. Za ku ba al'ummai da yawa rance, amma ba za ku bukaci rance don kanku ba. Za ku mallaki al'ummai da yawa, amma su ba za su mallake ku ba.

7. “Idan akwai wani danginku matalauci, a wani gari na cikin garuruwan ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, to, kada ku taurara zuciyarku, ku ƙi sakin hannu ga danginku matalauci.

8. Amma ku ba shi hannu sake, ku ranta masa abin da yake so gwargwadon bukatarsa.

9. Amma fa, ku lura, kada ku yi tunanin banza a zuciyarku, kuna cewa, ‘Ai, shekara ta bakwai, shekarar yafewa ta yi kusa,’ har ku ɗaure wa danginku matalauci fuska, ku ƙi ba shi kome. Zai yi kuka ga Ubangiji a kanku, abin kuwa zai zama laifi a kanku.

Karanta cikakken babi M. Sh 15