Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

L. Mah 14:17-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. Ta kuwa yi ta yi masa kuka har rana ta bakwai ta ƙarewar bikinsu. Amma a rana ta bakwai, ya faɗa mata amsar saboda yawan fitinarta. Ita kuwa ta faɗa wa mutanenta amsar ka-cici-ka-cicin.

18. A rana ta bakwai, kafin rana ta faɗi, mutanen garin suka ce masa,“Me ya fi zuma zaƙi?Me kuma ya fi zaki ƙarfi?”Ya kuwa ce musu,“Da ba don kun haɗa baki da matata ba,Da ba ku san amsar ka-cici-ka-cicin ɗin nan ba.”

19. Sa'an nan Ruhun Ubangiji ya sauko a kansa da iko, ya gangara zuwa Ashkelon. Ya kashe mutum talatin a can, ya kwashe ganima, ya ba waɗanda suka faɗa masa amsar ka-cici-ka-cicin riguna. Ya koma gida a husace saboda abin da ya faru.

20. Aka ɗauki matar Samson aka ba wanda ya yi masa abokin ango.

Karanta cikakken babi L. Mah 14