Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

L. Kid 5:18-23 Littafi Mai Tsarki (HAU)

18. Sa'an nan firist zai kwance gashin kanta, ya sa hadaya ta gari don tunawa a hannuwanta, hadayar gari ce ta kishi. Ya riƙe ruwan nan mai ɗaci da yake kawo la'ana a hannunsa.

19. Sa'an nan zai sa ta ta yi rantsuwa, ya ce mata, “Idan wani mutum bai kwana da ke ba, to, bari ki kuɓuta daga la'anar da ruwan nan mai ɗaci zai kawo.

20. Amma idan kin kwana da wani mutum wanda ba mijinki ba ne,

21. bari Ubangiji ya sa sunanki ya la'antu cikin jama'arki, ya sa cinyarki ta shanye, cikinki kuma ya kumbure.

22. Bari ruwan nan ya shiga cikinki, ya sa cikinki ya kumbure, cinyarki kuma ta shanye.”Sai matar ta amsa, ta ce, “Amin, amin, Ubangiji ya sa ya zama haka.”

23. Firist ɗin zai rubuta waɗannan la'anoni a cikin littafi sa'an nan ya wanke rubutun da ruwan nan mai ɗaci.

Karanta cikakken babi L. Kid 5