Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

L. Kid 27:15-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. Musa kuwa ya ce wa Ubangiji,

16. “Bari Ubangiji Allah na ruhohin dukan 'yan adam ya shugabantar da mutum a kan taron jama'ar,

17. mutumin da zai shugabance su cikin yaƙi, don kada taron jama'ar Ubangiji su zama kamar tumakin da ba su da makiyaya.”

18. Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ɗauki Joshuwa, ɗan Nun, mutumin da ya dace, ka ɗibiya masa hannuwanka,

19. ka sa shi ya tsaya a gaban Ele'azara, firist, da gaban dukan taron, sa'an nan ka keɓe shi a gabansu.

20. Ka danƙa masa ikonka don taron jama'ar Isra'ila su yi masa biyayya.

Karanta cikakken babi L. Kid 27