Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

L. Kid 26:52-63 Littafi Mai Tsarki (HAU)

52. Sai Ubangiji ya ce wa Musa,

53. “A raba wa waɗannan mutane gādon ƙasar bisa ga yawan kowace kabila.

54. Za ka ba babbar kabila babban rabo, ka ba ƙaramar kabila ƙaramin rabo. Kowace kabila za a ba ta gādo bisa ga yawanta.

55. Amma za a rarraba musu gādon ƙasar kabila kabila ta hanyar kuri'a.

56. Za a rarraba gādo tsakanin manya da ƙananan kabilai ta hanyar kuri'a.”

57. Waɗannan su ne Lawiyawan da aka ƙidaya bisa ga iyalansu, Gershon, da Kohat, da Merari.

58. Sauran iyalin Lawiyawa daga zuriyar Libni ne, da Hebron, da Mali, da Mushi, da Kora. Kohat shi ne mahaifin Amram,

59. wanda ya auri Yokabed 'yar Lawi wadda aka haifa masa a Masar. Yokabed ta haifa wa Amram, Haruna, da Musa, da Maryamu, 'yar'uwarsu.

60. Haruna yana da 'ya'ya huɗu maza, Nadab, da Abihu, da Ele'azara, da Itamar.

61. Amma Nadab da Abihu sun mutu saboda sun miƙa hadaya da haramtacciyar wuta a gaban Ubangiji.

62. Mazan da aka ƙidaya daga mai wata guda zuwa gaba sun kai dubu ashirin da dubu uku (23,000). Ba a haɗa jimillarsu tare da ta sauran Isra'ilawa ba, da yake ba a ba su gādo tare da su ba.

63. Waɗannan su ne Isra'ilawa waɗanda Musa da Ele'azara, firist, suka ƙidaya a filayen Mowab wajen Kogin Urdun daura da Yariko.

Karanta cikakken babi L. Kid 26