Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

L. Kid 24:18-25 Littafi Mai Tsarki (HAU)

18. Za a mallaki Edom,Hakka kuma za a mallaki Seyir abokiyar gābanta,Isra'ila za ta gwada ƙarfi.

19. Yakubu zai yi mulki,Zai hallaka waɗanda suka ragu cikin birni.”

20. Sai ya dubi Amalek, ya hurta jawabinsa, ya ce,“Amalek na fari ne cikin al'ummai,amm ƙarshensa hallaka ne.”

21. Sai kuma ya dubi Keniyawa, ya hurta jawabinsa, ya ce,“Wurin zamanku mai ƙarƙo ne,Gidajenku kuma suna cikin duwatsu.

22. Duk da haka za a lalatar da Keniyawa.Har yaushe za ku zama bayin Assuriyawa?”

23. Sai kuma ya hurta jawabinsa, ya ce,“Kaito, wa zai rayu sa'ad da Allah ya yi wannan?

24. Jiragen ruwa kuwa za su zo daga Kittim,Za su wahalar da Assuriya da Eber,Su kuma da kansu za su lalace.”

25. Sai Bal'amu ya tashi ya koma garinsu, Balak kuma ya yi tafiyarsa.

Karanta cikakken babi L. Kid 24