Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

L. Kid 22:19-28 Littafi Mai Tsarki (HAU)

19. Amma ina roƙonku ku kwana a nan yau har in san abin da Ubangiji zai faɗa mini.”

20. Sal Allah ya je wurin Bal'amu da dare, ya ce masa, “Idan mutanen nan sun zo kiranka ne, sai ka tashi, ka tafi tare da su, amma abin da na umarce ka kaɗai za ka yi.”

21. Da safe sai Bal'amu ya tashi ya yi wa jakarsa shimfiɗa, ya tafi tare da dattawan Mowab.

22. Allah kuwa ya husata don ya tafi, mala'ikan Ubangiji ya tsaya a hanya ya tarye shi. Shi kuwa yana tafe a bisa jakarsa tare da barorinsa biyu.

23. Da jakar ta ga mala'ikan Ubangiji yana tsaye kan hanya da takobi zare a hannunsa, sai ta kauce daga hanya, ta shiga saura. Bal'amu kuwa ya buge ta don ya komar da ita a hanyar.

24. Sai mala'ikan Ubangiji ya je, ya tsaya a inda hanyar ta yi matsatsi a tsakanin bangayen gonakin inabi.

25. Sa'ad da jakar ta ga mala'ikan Ubangiji, ta matsa a jikin bango, ta goge ƙafar Bal'amu ga bangon, sai ya sāke bugunta.

26. Mala'ikan Ubangiji kuma ya sha kanta, ya tsaya a ƙunƙuntaccen wuri inda ba wurin juyawa zuwa dama ko hagu.

27. Da jakar ta ga mala'ikan Ubangiji, sai ta kwanta a ƙafafun Bal'amu. Sai Bal'amu ya husata, ya bugi jakar da sandansa.

28. Ubangiji kuwa ya buɗe bakin jakar, ta ce wa Bal'amu, “Me na yi maka, da ka buge ni har sau uku?”

Karanta cikakken babi L. Kid 22