Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

L. Kid 10:8-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. 'Ya'yan Haruna, maza, firistoci, su ne za su busa kakakin.“Kakakin za su zama muku ka'ida ta din din din cikin dukan zamananku.

9. Sa'ad da kuka tafi yaƙi a ƙasarku gāba da maƙiyanku da suke matsa muku lamba, sai ku yi busar faɗakarwan nan da kakakin, Ubangiji Allahnku zai tuna da ku, ya cece ku daga maƙiyanku.

10. A ranar murnarku, da lokacin ƙayyadaddun idodinku, da tsayawar watanninku, za ku busa kakakin a lokacin yin hadayunku na ƙonawa, da hadayunku na salama. Za su zama sanadin tunawa da ku a gaban Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.”

11. A rana ta ashirin ga watan biyu a shekara ta biyu, sai aka gusar da girgijen daga kan alfarwa ta sujada.

12. Isra'ilawa kuwa suka tashi daki-daki daga jejin Sinai. Girgijen kuma ya tsaya a jejin Faran.

13. Suka fara tafiyarsu bisa ga umarnin da Ubangiji ya yi wa Musa.

14. Tutar zangon kabilar mutanen Yahuza ta fara tashi, ƙungiyoyinsu suna biye. Nashon, ɗan Amminadab, shi ne shugaban rundunarsu.

15. Shugaban rundunar kabilar mutanen Issaka Netanel ne, ɗan Zuwar.

Karanta cikakken babi L. Kid 10