Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

L. Fir 23:23-34 Littafi Mai Tsarki (HAU)

23. Ubangiji ya yi magana da Musa, cewa,

24. ya ce wa Isra'ilawa su mai da rana ta fari ga wata na bakwai ta zama ranar hutu musamman, sa'ad da za su ji busar ƙaho, sai su taru domin yin sujada.

25. Ba za su yi aiki mai wuya ba. Za su miƙa hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji.

26. Ubangiji ya yi magana da Musa, cewa,

27. rana ta goma ga watan bakwai za ta zama rana ta yin kafara da lokacin yin muhimmin taro. Kada su ci abinci a ranar, su taru su yi sujada, su miƙa hadaya taƙonawa ga Ubangiji.

28. Ba za su yi aiki a wannan rana ba, gama rana ce ta yin kafara dominsu.

29. Duk wanda ya ci abinci a wannan rana ba za a lasafta shi ɗaya daga cikin jama'ar Allah ba.

30. Duk kuma wanda ya yi aiki a wannan rana, Ubangiji kansa zai kashe shi.

31. Wannan ka'ida ta shafi dukan zuriyarsu a duk inda suke.

32. Daga faɗuwar ranar tara ga watan, har zuwa faɗuwar ranar goma ga watan, su kiyaye wannan ta zama ranar hutu musamman. A wannan lokaci ba wanda zai ci abinci.

33. Ubangiji kuma ya yi magana da Musa, ya ce ya faɗa wa Isra'ilawa, cewa,

34. a rana ta goma sha biyar ga watan bakwai za a yi Idin Bukkoki kwana bakwai saboda Ubangiji.

Karanta cikakken babi L. Fir 23