Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

L. Fir 21:14-24 Littafi Mai Tsarki (HAU)

14. Kada ya auri mace wadda mijinta ya rasu, ko sakakkiya, ko karuwa, amma ya auri budurwa daga cikin kabilarsa,

15. domin kada ya ƙazantar da 'ya'yansa waɗanda ya kamata su zama tsarkakakku. Ni ne Ubangiji, na kuwa keɓe shi ya zama babban firist.”

16. Sai Ubangiji ya umarce Musa

17. ya faɗa wa Haruna cewa, “Kada ko ɗaya daga cikin zuriyarka, da yake da lahani ya kusato garin ya miƙa hadaya ta ci gare ni har abada.

18. Duk mutumin da yake da lahani na makanta, ko gurguntaka, ko rauni a fuska, ko gaɓar da ta fi wata,

19. ko tauyayye a ƙafa ko a hannu,

20. ko mai ƙusumbi, ko wada, ko mai lahani a ido, ko cuta mai sa ƙaiƙayi, ko kirci, ko dandaƙaƙƙe, ba zai kusato garin ya miƙa hadaya ba.

21. Duk mutumin da yake cikin zuriyar Haruna firist, wanda yake da lahani, ba zai kusato garin ya miƙa hadaya ta ci gare ni ba.

22. Amma zai iya ci daga cikin tsattsarkan abincin da aka miƙa mini, da abinci mafi tsarki.

23. Sai dai ba zai kusaci labulen, ko ya tafi kusa da bagaden ba, domin yana da lahani, don kada ya ɓata wuraren yin sujada, gama ni ne Ubangiji, ni kuwa na tsarkake su.”

24. Haka nan kuwa Musa ya faɗa wa Haruna, da 'ya'yan Haruna, maza, da dukan Isra'ilawa.

Karanta cikakken babi L. Fir 21