Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

L. Fir 20:4-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

4. Idan kuwa mutanen ƙasar ba su kashe mutumin nan, wanda ya ba Molek ɗaya daga cikin 'ya'yansa ba,

5. ni kaina zan yi gāba da mutumin nan da iyalinsa, da waɗanda suka yarda suka bi Molek tare da shi. Ba zan ƙara ce da su mutanena ba.

6. “Duk wanda yake sha'ani da masu mabiya, ko da bokaye zan yi gāba da wannan mutum, in raba shi da jama'arsa.

7. Sai ku kiyaye kanku da tsarki, gama ni ne Ubangiji Allahnku.

8. Ku kuma kiyaye dokokina, ku aikata su, gama ni ne Ubangiji wanda ya keɓe ku.

9. “Dukan wanda ya zagi mahaifinsa, ko mahaifiyarsa za a kashe shi, gama ya zagi mahaifinsa da mahaifiyarsa. Alhakin jininsa yana wuyansa.

Karanta cikakken babi L. Fir 20