Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

L. Fir 15:1-10 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ubangiji ya ba Musa da Haruna waɗannan ka'idodi

2. domin jama'ar Isra'ila. Duk lokacin da wani namiji yake ɗiga daga al'aurarsa, ƙazantacce ne.

3. Ko al'aurar tana ɗiga ko ta daina shi dai ƙazantacce ne.

4. Kowane gado da mai ɗigan ya kwanta a kai ya ƙazantu, da kowane abu da ya zauna a kai ya ƙazantu.

5. Duk wanda ya taɓa gadonsa, sai ya wanke tufafinsa, ya yi wanka da ruwa, zai ƙazantu har maraice.

6. Duk wanda kuma ya zauna a kan kowane abin da mai ɗigar ya zauna a kai, sai ya wanke tufafinsa, ya yi wanka da ruwa, zai ƙazantu har maraice.

7. Wanda kuma ya taɓa jikin mai ɗigar, sai ya wanke tufafinsa ya yi wanka da ruwa, zai ƙazantu har maraice.

8. Idan mai ɗigar ya tofar da yau a kan wanda yake da tsabta, sai mutumin ya wanke tufafinsa, ya yi wanka da ruwa, zai ƙazantu har maraice.

9. Kowane sirdi da mai ɗigar ya zauna a kai zai ƙazantu.

10. Duk wanda ya taɓa kowane abin da yake ƙarƙashin sirdin zai ƙazantu har maraice, duk kuma wanda ya ɗauki wannan abu, sai ya wanke tufafinsa, ya yi wanka da ruwa, zai ƙazantu har maraice.

Karanta cikakken babi L. Fir 15