Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

K. Mag 19:14-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

14. Mutum na iya cin gādon gida da kuɗi daga wurin iyayensa, amma Ubangiji ne kaɗai yake ba shi mace mai hankali.

15. Rago, yi ta ragwancinka ka yi ta sharar barci, amma kai za ka sha yunwa.

16. Ka kiyaye umarnai za ka rayu, in ka ƙi binsu kuwa za ka mutu.

17. Sa'ad da ka bayar ga matalauci kamar ka ba Ubangiji rance ne, gama Ubangiji zai sāka maka.

18. Ka yi wa 'ya'yanka tarbiyya tun suna ƙanana yadda za su iya koyo. Idan ba ka yi haka ba, ka taimaka wajen lalacewarsu ke nan.

19. Idan mutum mai zafin rai ne, ƙyale shi ya sha sakamakonsa. Idan ka fisshe shi daga cikin wahala sau ɗaya, sai ka sāke yi.

20. Ka saurari shawara, ka yarda ka koya, wata rana za ka zama mai hikima.

21. Mutum ya iya shirya dabaru iri iri, amma sai nufin Ubangiji ne zai tabbata.

Karanta cikakken babi K. Mag 19