Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

K. Mag 11:15-31 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. Wanda ya ɗaukar wa baƙo lamuni zai yi da na sani, zai fi maka sauƙi idan ba ruwanka.

16. Mace mai mutunci abar girmamawa ce, amma azzalumai za su sami dukiya.

17. In ka yi alheri, kanka ka samar wa tagomashi, in kuwa ka yi mugunta, kanka ka cutar.

18. A ainihi mugaye ba su cin ribar kome, amma idan ka yi abin da yake daidai, ka tabbata za a sāka maka da alheri.

19. Mutumin da ya yi niyyar aikata abin da yake daidai zai rayu, amma mutumin da ya dukufa ga aikata mugunta zai mutu.

20. Ubangiji yana ƙin masu muguwar niyya, amma yana murna da waɗanda suke aikata abin da yake daidai!

21. Ka tabbata fa za a hukunta mugaye, amma ba za a hukunta adalai ba.

22. Kome kyan mace idan ba ta da kangado, tana kamar zoben zinariya a hancin alade.

23. Abin da mutanen kirki suke so kullum yakan jawo alheri, idan mugaye sun sami biyan bukatarsu kowa zai yi ɓacin rai.

24. Waɗansu mutane sukan kashe kuɗinsu hannu sake, duk da haka arzikinsu sai ƙaruwa yake yi. Waɗansu kuwa saboda yawan tsumulmularsu sukan talauce.

25. Ka yi alheri za ka arzuta. Ka taimaki waɗansu, su kuma za su taimake ka.

26. Mutane sukan la'anci mai ɓoye hatsi, yana jira ya yi tsada, amma sukan yabi wanda yake sayar da nasa.

27. Idan nufe-nufenka na kirki ne za a girmama ka, amma idan kai mai neman tashin hankali ne, to, abin da zai same ka ke nan.

28. Adalai za su arzuta, kamar ganyaye da bazara, amma waɗanda suke dogara ga dukiyarsu za su karkaɗe kamar ganyaye da kaka.

29. Mutumin da yake jawo wa iyalinsa wahala, ƙarshensa talaucewa. Wawaye za su zama barorin masu hikima a ko yaushe.

30. Adalci yana rayar da mutum, wanda yake da hikima kuma yakan ceci rayuka.

31. Idan an sāka wa mutumin kirki da alheri a duniya, hakika za a hukunta wa mugaye da masu zunubi.

Karanta cikakken babi K. Mag 11