Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Josh 9:24-27 Littafi Mai Tsarki (HAU)

24. Sai suka amsa wa Joshuwa, suka ce, “Domin bayinka sun ji labari Ubangiji Allahnka ya umarci bawansa Musa ya ba ku ƙasar duka, ku hallaka dukan mazaunan ƙasar a gabanku, don haka muka ji tsoronku ƙwarai saboda rayukanmu, shi ya sa muka yi haka.

25. Yanzu dai muna a hannunka, ka yi yadda ka ga ya yi maka kyau.”

26. Haka kuwa ya yi musu, ya cece su daga hannun Isra'ilawa, har ba su kashe su ba.

27. Amma Joshuwa ya sa su su zama masu saro itace da masu ɗebo ruwa domin jama'a da bagaden Ubangiji. Zai zama aikinsu na yau da kullum a wurin da Ubangiji zai zaɓa.

Karanta cikakken babi Josh 9