Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Josh 4:14-18 Littafi Mai Tsarki (HAU)

14. A ranan nan Ubangiji ya ɗaukaka Joshuwa a idon dukan Isra'ilawa, har suka ga kwarjininsa dukan kwanakin ransa kamar yadda suka ga na Musa.

15. Ubangiji kuma ya ce wa Joshuwa,

16. “Ka umarci firistocin da suke ɗauke da akwatin shaida, su fito daga cikin Urdun.”

17. Sai Joshuwa ya umarci firistocin su fito daga cikin Urdun.

18. Da firistocin da suke ɗauke da akwatin alkawari na Ubangiji suka fito daga tsakiyar Urdun, suka taka sandararriyar ƙasa, sai ruwan Urdun ya malalo ya tumbatsa kamar dā.

Karanta cikakken babi Josh 4