Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Josh 19:16-24 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. Waɗannan su ne garuruwa da ƙauyukansu da suke cikin gādon mutanen Zabaluna bisa ga iyalansu.

17. Kuri'a ta huɗu ta faɗo a kan kabilar Issaka bisa ga iyalanta.

18. Garuruwan da suke cikin yankin ƙasar su ne, Yezreyel, da Kesullot, da Shunem,

19. da Hafarayim, da Shiyon, da Anaharat,

20. da Rabbit, da Kishiyon, da Ebez,

21. da Remet da En-ganim, da En-hadda, da Bet-fazzez.

22. Iyakar kuma ta bi ta Tabor, da Shahazuma, da Bet-shemesh. Sa'an nan ta gangara a Kogin Urdun. Akwai garuruwa goma sha shida da ƙauyukansu.

23. Waɗannan su ne garuruwa da ƙauyukansu da suke a yankin ƙasar da kabilar Issaka ta gāda bisa ga iyalanta.

24. Kuri'a ta biyar ta fāɗo a kan kabilar Ashiru bisa ga iyalanta.

Karanta cikakken babi Josh 19