Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Josh 10:9-18 Littafi Mai Tsarki (HAU)

9. Sai Joshuwa ya tafi ya auka musu ba labari, gama daga Gilgal ya bi dare zuwa can.

10. Ubangiji kuwa ya sa suka gigice a gaban Isra'ilawa. Isra'ilawa suka kashe su da yawa a Gibeyon, suka runtume su ta hanyar haurawa zuwa Bet-horon. Suka yi ta karkashe su har zuwa Azeka da Makkeda.

11. Sa'ad da suke gudun Isra'ilawa suna a gangarar hawan Bet-horon, sai Ubangiji ya jefe su da manyan duwatsu daga sama, har zuwa Azeka, suka mutu. Waɗanda suka mutu ta ƙanƙarar duwatsu sun fi waɗanda Isra'ilawa suka kashe da takobi.

12. Sa'an nan Joshuwa ya yi magana da Ubangiji a gaban Isra'ilawa a ranar da Ubangiji ya ba da Amoriyawa gare su, ya ce,“Ke rana, ki tsaya a Gibeyon,Kai kuma wata, ka tsaya a kan kwarin Ayalon.”

13. Sai rana ta tsaya cik, wata kuma ya tsaya,Har al'ummar ta ɗauki fansa a kan abokan gābansu.Ai, wannan a rubuce yake a littafin Yashar. Rana dai ta tsaya a tsaka, ta yi jinkirin faɗuwa da misalin yini guda.

14. Ba a taɓa yin yini kamar wannan ba, ko kafin wannan yini, ko bayansa kuma, da Ubangiji ya saurari muryar mutum. Gama Ubangiji ya yi yaƙi domin Isra'ilawa.

15. Sa'an nan Joshuwa ya koma zango a Gilgal tare da dukan Isra'ilawa.

16. Waɗannan sarakuna biyar kuma suka gudu, suka ɓuya a cikin kogo a Makkeda.

17. Aka faɗa wa Joshuwa cewa, “An sami sarakunan nan biyar, sun ɓuya a kogo a Makkeda.”

18. Sai Joshuwa ya ce, “Ku mirgina manyan duwatsu, ku rufe bakin kogon, sa'an nan ku sa mutane su yi tsaronsu.

Karanta cikakken babi Josh 10