Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ish 48:13-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

13. Dantsena ne ya kafa harsashin ginin duniya,Ya kuma shimfiɗa sammai.Lokacin da na kira duniya da sararin sama,Sukan zo nan da nan, su gabatar da kansu!

14. “Ku tattaru, ku duka, ku kasa kunne!Ba ko ɗaya cikin alloli da zai iya yin annabci ba,Cewa mutumin da na zaɓa, shi zai iya fāɗa wa Babila,Zai yi abin da na umarce shi.

15. Ni ne na yi magana, na kuwa kira shi,Na yi masa jagora na kuwa ba shi nasara.

16. “Yanzu fa, sai ku matso kusa da ni,Ku ji abin da nake faɗa.Tun da farko na yi magana da ku a fili,A koyaushe nakan cika maganata.”(Yanzu Ubangiji Allah ya ba ni iko, ya kuwa aike ni.)

17. Allah Mai Tsarki na Isra'ila,Ubangiji, wanda ya fanshe ku, ya ce,“Ni ne Ubangiji Allahnku,Wanda yake so ya koya muku domin amfanin kanku,Ya kuwa nuna muku hanyar da za ku bi.

Karanta cikakken babi Ish 48