Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ish 41:8-18 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. “Amma kai, Isra'ila bawana,Kai ne jama'ar da na zaɓa,Zuriyar Ibrahim, abokina,

9. Na kawo ka daga maƙurar duniya,Na kira ka daga kusurwoyi mafi nisa.Na ce maka, ‘Kai ne bawana.’Ban ƙi ka ba, amma maimakon haka na zaɓe ka.

10. Kada ka ji tsoro, ina tare da kai,Ni ne Allahnka, kada ka bar kome ya firgita ka.Zan sa ka yi ƙarfi, in kuma taimake ka,Zan kiyaye ka, in cece ka.

11. “Su waɗanda suke fushi da ku, ku jama'ata,Za a ƙasƙantar da su su ji kunya.Waɗanda suke faɗa da ku kuwa za su mutu.

12. Za ku neme su, amma ba za ku same su ba,Wato waɗanda suke gāba da ku.Waɗanda suka kama yaƙi da ku,Za su shuɗe daga duniya.

13. Ni ne Ubangiji Allahnku,Na ƙarfafa ku, na kuwa faɗa muku,‘Kada ku ji tsoro, ni zan taimake ku.’ ”

14. Ubangiji ya ce,“Isra'ila, ku kima ne marasa ƙarfi kuma,Kada ku ji tsoro, zan taimake ku.Ni Allah Mai Tsarki na Isra'ila, ni ne mai fansarku.

15. Zan sa ku zama kamar abin sussuka,Wanda yake sabo, mai kaushi, mai tsini.Za ku sussuke duwatsu ku lalatar da su,Za a marmashe tuddai kamar ƙura.

16. Za ku watsa su sama cikin iska,Iska za ta hure su, ta tafi da su,Hadiri kuma zai warwatsar da su.Amma za ku yi murna, gama ni ne Allahnku,Za ku yabe ni, Allah Mai Tsarki na Isra'ila.

17. “Sa'ad da jama'ata ta bukaci ruwa,Sa'ad da maƙogwaronsu ya bushe da ƙishi,Sa'an nan ni Ubangiji, zan amsa addu'arsu,Ni Allah na Isra'ila, ba zan taɓa yashe su ba.

18. Zan sa kogunan ruwa su yi gudu daga ƙeƙasassun tuddai,Maɓuɓɓugan ruwa su yi gudu a kwaruruka.Zan sa hamada ta zama kududdufan ruwa,Busasshiyar ƙasa kuma ta zama maɓuɓɓugan ruwa.

Karanta cikakken babi Ish 41