Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ish 41:25-27 Littafi Mai Tsarki (HAU)

25. “Na zaɓi mutum wanda yake zaune a gabas,Zan kawo shi don ya kawo hari daga arewa.Zai tattake masu mulki su zama kamar lāka,Kamar yadda magini yake tattake yumɓu.

26. Wane ne a cikinku ya faɗa mana tun da wuri,Ko ya yi annabci, cewa wannan zai faru,Har da za mu ce kun yi daidai?Ba ko ɗayanku da ya ce tak a kan wannan,Ba kuwa wanda ya ji kuna faɗar wani abu!

27. Ni Ubangiji, ni ne na farko da na faɗa wa Sihiyona albishir,Na aiki manzo zuwa Urushalima don ya ce,‘Jama'arki suna zuwa! Suna zuwa gida.’

Karanta cikakken babi Ish 41