Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ish 40:1-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ubangiji ya ce,“Ka ta'azantar da jama'ata.Ka ta'azantar da su!

2. Ka ƙarfafa jama'ar Urushalima.Ka faɗa musu sun sha wahala, ta isa,Yanzu kuwa an gafarta musu zunubansu.Na yi musu cikakken hukunci saboda dukan zunubansu.”

3. Murya tana kira tana cewa,“Ka shirya hanya a jeji domin Ubangiji!Ka share hanya a hamada domin Allahnmu!

4. Za a cike kowane kwari,Za a baje kowane dutse.Tuddai za su zama fili,Ƙasa mai kururrumai za ta zama sumul.

5. Sa'an nan za a bayyana ɗaukakar Ubangiji,Dukan 'yan adam kuwa za su gan ta.Ubangiji ne kansa ya yi wannan alkawari.”

6. Murya ta yi kira ta ce, “Ka yi shela!”Na yi tambaya na ce, “Shelar me zan yi?”“Ka yi shela, cewa dukan 'yan adam kamar ciyawa suke,Ba su fi furannin jeji tsawon rai ba.

Karanta cikakken babi Ish 40