Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ish 26:6-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Waɗanda aka zalunta, a kansa suke tafiya yanzu,Suna tattaka shi da ƙafafunsu.

7. Ka sa hanyar mutanen kirki ta yi sumul,Hanyar da suke bi ta yi bai ɗaya,

8. Muna bin nufinka, muna sa zuciya gare ka.Kai kaɗai ne bukatarmu.

9. Da dare ina zuba ido gare ka da zuciya ɗaya.Sa'ad da kake yi wa duniya da jama'arta shari'aDukansu za su san yadda adalci yake.

10. Ko da yake kana yi wa mugaye alheri,Duk da haka ba su taɓa koyon abin da yake na kirki ba.Har a nan ma, a ƙasar adalai,Suna ta aikata kuskure,Sun ƙi ganin girmanka.

11. Maƙiyanka ba su san za ka hukunta su ba.Ya Ubangiji, ka kunyatar da su, ka sa su sha wahala,Wato su sha wahalar hukuncin da ka shirya.Ka nuna musu yawan ƙaunar da kake yi wa jama'arka.

Karanta cikakken babi Ish 26