Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ish 26:2-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

2. A buɗe ƙofofin birnin,A bar amintacciyar al'umma ta shiga,Al'ummar da jama'arta take aikata abin da yake daidai.

3. Kai kake ba da cikakkiyar salama, ya Ubangiji,Ga waɗanda suke riƙe da manufarsu da ƙarfi,Waɗanda suke dogara gare ka.

4. Ku dogara ga Ubangiji har abada.Zai kiyaye mu kullayaumin.

5. Ya ƙasƙantar da masu girmankai,Ya hallaka ƙaƙƙarfan birnin da suke zaune ciki,Ya rusa garunsa ƙasa.

6. Waɗanda aka zalunta, a kansa suke tafiya yanzu,Suna tattaka shi da ƙafafunsu.

7. Ka sa hanyar mutanen kirki ta yi sumul,Hanyar da suke bi ta yi bai ɗaya,

8. Muna bin nufinka, muna sa zuciya gare ka.Kai kaɗai ne bukatarmu.

9. Da dare ina zuba ido gare ka da zuciya ɗaya.Sa'ad da kake yi wa duniya da jama'arta shari'aDukansu za su san yadda adalci yake.

10. Ko da yake kana yi wa mugaye alheri,Duk da haka ba su taɓa koyon abin da yake na kirki ba.Har a nan ma, a ƙasar adalai,Suna ta aikata kuskure,Sun ƙi ganin girmanka.

11. Maƙiyanka ba su san za ka hukunta su ba.Ya Ubangiji, ka kunyatar da su, ka sa su sha wahala,Wato su sha wahalar hukuncin da ka shirya.Ka nuna musu yawan ƙaunar da kake yi wa jama'arka.

12. Kai za ka wadata mu, ya Ubangiji,Duk abin da muka iya yi daga gare ka ne.

13. Ya Ubangiji Allahnmu, waɗansu sun mallake mu,Amma kai kaɗai ne Ubangijinmu.

14. Yanzu kuwa sun mutu, ba za su ƙara rayuwa ba,Kurwarsu ba za ta tashi ba,Domin ka hukunta su, ka hallaka su.Ba wanda zai ƙara tunawa da su.

15. Ya Ubangiji, ka sa al'ummarmu ta yi ƙarfi,Ka faɗaɗa karkararta a kowane gefe,Wannan kuwa ya sa ana girmama ka.

16. Ka hukunta jama'arka, ya Ubangiji,A cikin azaba sun yi addu'a gare ka.

17. Kai ne, ya Ubangiji, ka sa muka yi kuka,Kamar macen da take naƙuda tana kuka da azaba.

Karanta cikakken babi Ish 26