9. Ku ba Mowab fikafikai,Gama za ta tashi ta gudu,Garuruwanta za su zama kango,Ba mazauna cikinsu.
10. “La'ananne ne shi wanda yake yinaikin Ubangiji da ha'inci,La'ananne ne shi kuma wanda yahana wa takobinsa jini.
11. “Tun daga ƙuruciya Mowab tanazama lami lafiya,Hankali kwance,Ba a jujjuya ta daga tulu zuwa tuluba,Ba a taɓa kai ta bauta ba,Domin haka daɗin ɗanɗanonta bairabu da ita ba,Ƙanshinta kuma bai sāke ba.”
12. Ubangiji ya ce, “Domin haka kwanaki suna zuwa, sa'ad da zai aika da mutane su tuntsurar da tuluna, su zubar da ruwan inabi, su farfasa tulunanta.