Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Irm 48:4-14 Littafi Mai Tsarki (HAU)

4. “An hallakar da Mowab,Ƙanananta suna kuka.

5. Gama a hawan Luhit, za su hau dakuka,Gama a gangaren Horonayim,Suna jin kukan wahalar halaka.

6. Ku gudu don ku tserar darayukanku,Ku gudu kamar jakin jeji.

7. “Kun dogara ga ƙarfinku dawadatarku,Amma yanzu za a ci ku da yaƙi,Kemosh zai tafi bautaTare da firistocinsa dashugabanninsa.

8. Mai hallakarwa zai shiga kowanegari,Don haka ba garin da zai tsira.Kwari da tudu za su lalace,Ni Ubangiji na faɗa.

9. Ku ba Mowab fikafikai,Gama za ta tashi ta gudu,Garuruwanta za su zama kango,Ba mazauna cikinsu.

10. “La'ananne ne shi wanda yake yinaikin Ubangiji da ha'inci,La'ananne ne shi kuma wanda yahana wa takobinsa jini.

11. “Tun daga ƙuruciya Mowab tanazama lami lafiya,Hankali kwance,Ba a jujjuya ta daga tulu zuwa tuluba,Ba a taɓa kai ta bauta ba,Domin haka daɗin ɗanɗanonta bairabu da ita ba,Ƙanshinta kuma bai sāke ba.”

12. Ubangiji ya ce, “Domin haka kwanaki suna zuwa, sa'ad da zai aika da mutane su tuntsurar da tuluna, su zubar da ruwan inabi, su farfasa tulunanta.

13. Sa'an nan Kemosh zai kunyatar da Mowab, kamar yadda Betel wadda Isra'ilawa suka dogara gare ta ta kunyatar da su.

14. “Don me kake cewa,‘Mu jarumawa ne, mayaƙan gaske?’

Karanta cikakken babi Irm 48