Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Irm 4:26-31 Littafi Mai Tsarki (HAU)

26. Na duba, sai na ga ƙasa mai dausayita zama hamada,An mai da dukan biranentakangwayeA gaban Ubangiji saboda zafinfushinsa.

27. Gama Ubangiji ya ce, “Ƙasar duka za ta zama kufai, amma duk da haka, ba wannan ne zai zama ƙarshenta na har abada ba.

28. Duniya za ta yi makoki sabodawannan,Sammai za su duhunta,Gama ni na faɗa, haka kuwa na nufain yi,Ba zan ji tausayi ba,Ba zan kuwa fāsa ba.”

29. Da jin motsin mahayan dawakai dana maharbaKowane gari zai fashe.Waɗansu za su shiga kurama,Waɗansu kuma su hau kan duwatsu.Dukan birane za su fashe tas,Ba wanda zai zauna a cikinsu.

30. Ya ke da kike kufai marar kowa,Me kike nufi da kika ci ado da mulufi,Kike caɓa ado da kayan zinariya,Kika sa wa idanunki tozali ram?Kin yi kwalliyarki a banza,Abokan sha'anin karuwancinki sunraina ki,Ranki suke nema.

31. Na ji kuka kamar na mace wadda takenaƙuda,Na ji nishi kamar na mace a lokacinhaihuwarta ta fari,Na ji kukan 'yar Sihiyona tanakyakyari,Tana miƙa hannuwanta tana cewa,“Wayyo ni kaina, gama ina suma agaban masu kisankai!”

Karanta cikakken babi Irm 4