Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Irm 4:15-26 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. Gama wata murya daga Dan tafaɗa,Ta kuma yi shelar masifar da za tafito daga duwatsun Ifraimu.

16. “A faɗakar da al'ummai, yana zuwa,A faɗa wa Urushalima cewa,‘Masu kawo mata yaƙi suna zuwadaga ƙasa mai nisa,Suna yi wa biranen Yahuza ihu.

17. Za su kewaye Yahuza kamar masutsaron saura,Saboda ta tayar wa Ubangiji.’ NiUbangiji na faɗa.

18. “Al'amuranki da ayyukanki sukajawo miki wannan halaka,Tana da ɗaci kuwa,Ta soki har can cikin zuciyarki.”

19. Azaba! Ba zan iya daurewa da azababa!Zuciyata! Gabana yana faɗuwa daƙarfi,Ba zan iya yin shiru ba,Gama na ji amon ƙaho da hargowaryaƙi.

20. Bala'i a kan bala'i,Ƙasa duka ta zama kufai,An lalatar da alfarwaina, ba zato batsammani,Labulena kuwa farat ɗaya.

21. Har yaushe zan yi ta ganin tuta,In yi ta jin amon ƙaho?

22. Ubangiji ya ce,“Mutanena wawaye ne,Ba su san ni ba,Yara ne dakikai,Ba su da ganewa.Suna gwanance da aikin mugunta,Amma ba su san yadda za su yinagarta ba.”

23. Da na duba duniya sai na ga kufai cekawai ba kome,Na kuma dubi sammai sai na ga bahaske.

24. Da na duba duwatsu, sai na ga sunamakyarkyata,Dukan tuddai kuma suna rawar jiki,su yi gaba su yi baya.

25. Na duba sai na ga ba ko mutumɗaya,Dukan tsuntsaye kuma sun tsere.

26. Na duba, sai na ga ƙasa mai dausayita zama hamada,An mai da dukan biranentakangwayeA gaban Ubangiji saboda zafinfushinsa.

Karanta cikakken babi Irm 4