Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Irm 33:1-4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ubangiji ya sāke yin magana da Irmiya sa'ad da yake a kulle a gidan waƙafi.

2. Ubangiji wanda ya halitta duniya, ya siffata ta, ya kafa ta, sunansa Ubangiji, ya ce,

3. “Ka kira ni, ni kuwa zan amsa maka, zan kuwa nuna maka manyan al'amura masu girma da banmamaki, waɗanda ba ka sani ba.”

4. Gama haka Ubangiji, Allah na Isra'ila, ya ce, a kan gidajen da suke a wannan birni, da gidajen sarakunan Yahuza, waɗanda aka rurrushe domin a yi wa garukan jigo saboda mahaurai da suka kewaye birni, da kuma saboda yaƙi.

Karanta cikakken babi Irm 33