Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Irm 3:1-6 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Ubangiji ya ce,“Idan mutum ya saki matarsa,Ta kuwa rabu da shi, har ta auriwani,Ya iya ya komo da ita?Ashe, yin haka ba zai ƙazantar daƙasar ba?Ya Isra'ila, kin yi karuwanci,Abokan sha'anin karuwancinki, sunada yawa.Za ki sāke komowa wurina?Ni, Ubangiji, na faɗa.

2. Ki ta da idonki, ki duba filayentuddai ki gani,Akwai wurin da ba ki laɓe kin yikaruwanci ba?Kin yi ta jiran abokan sha'aninkaruwancinki a kan hanya,Kamar Balaraben da yake fako ahamada.Kin ƙazantar da ƙasar da mugunkaruwancinki.

3. Saboda haka aka ƙi yin ruwa,Ruwan bazara bai samu ba.Goshinki irin na karuwa ne, ba ki jinkunya.

4. “Yanzu kin ce, ‘Kai ne mahaifina,Ka ƙaunace ni tun ina cikinƙuruciyata.

5. Za ka dinga yin fushi da ni?Za ka husata da ni har abada?’Ga shi, ke kika faɗa, amma ga shi,kin aikata dukan muguntar dakika iya yi.”

6. A zamanin sarki Yosiya, Ubangiji ya ce mini, “Ka ga abin da take yi, ita marar amincin nan, wato Isra'ila? Yadda a kowane tudu mai tsayi, da a gindin kowane itace mai duhuwa, a wurare ne ta yi karuwancinta.

Karanta cikakken babi Irm 3