Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Irm 23:29-36 Littafi Mai Tsarki (HAU)

29. Maganata kamar wuta ce, kamar guduma mai farfashe dutse. Ni Ubangiji na faɗa.

30. Domin haka, ga shi, ina gāba da annabawan da suke satar maganata daga wurin junansu. Ni Ubangiji na faɗa.

31. Ina kuma gāba da annabawan da suke faɗar ra'ayin kansu, sa'an nan su ce, ‘Ubangiji ne ya faɗa.’

32. Ina kuma gāba da annabawan da suke annabcin mafarkansu na ƙarya, suna kuwa faɗarsu suna ɓad da mutanena da ƙarairayinsu, saboda rashin hankalinsu. Ni ban aike su ba, ban kuwa umarce su ba. Ba su amfani wannan jama'a ba ko kaɗan, ni Ubangiji na faɗa.”

33. “Kai Irmiya, sa'ad da wani mutum daga cikin mutanen nan, ko annabi, ko firist ya tambaye ka cewa, ‘Mece ce nawayar Ubangiji?’ Sai ka ce masa, ‘Ku ne nawayar, zan kuwa rabu da ku,’ ni Ubangiji na faɗa.

34. Idan annabi ko firist, ko wani daga cikin jama'a, ya ce, ‘Nawayar Ubangiji,’ zan hukunta shi duk da iyalin gidansa.

35. Haka kowannenku zai ce wa maƙwabcinsa da ɗan'uwansa, ‘Wace amsa Ubangiji ya bayar? Me Ubangiji ya faɗa?’

36. Amma ba za ku ƙara ambatar nawayar Ubangiji ba, gama maganar kowane mutum za ta zama nawaya, ga shi, kun ɓata maganar Allah mai rai, Ubangiji Mai Runduna, Allahnmu.

Karanta cikakken babi Irm 23