Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Irm 18:17-22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

17. Haka zan warwatsa suKamar yadda iskar gabas take yi, agaban abokan gābansu,Zan juya musu baya, ba za su gafuskata ba,A ranar masifarsu.’ ”

18. Sa'an nan suka ce, “Zo mu shirya wa Irmiya maƙarƙashiya, gama firist ba zai bar bin shari'a ba. Haka nan ma masu hikima ba za su bar yin shawara ba, haka nan kuma annabi ba zai bar yin magana ba! Ku zo mu kai ƙararsa, kada mu kula da abin da zai faɗa.”

19. Irmiya kuwa ya yi addu'a ya ce,“Ya Ubangiji, ka kasa kunne gare ni,ka ji ƙarar maƙiyana!

20. Daidai ne a rama alheri damugunta?Duk da haka sun kafa wa raina tarko.Ka tuna yadda na tsaya a gabanka,Na yi maganar alheri a kansu,Domin ka janye fushinka daga garesu.

21. Saboda haka ka kawo wa 'ya'yansuyunwa,Ka bashe su ga takobi,Bari matansu su rasa 'ya'ya,mazansu su mutu,Ka sa annoba ta kashe mazansu,A kashe samarinsu da takobi ayaƙi.

22. Bari a ji kururuwa daga gidajensu,Saboda maharan da ka aika musufarat ɗaya,Gama sun haƙa rami don in fāɗa,Sun kafa wa ƙafafuna tarkuna.

Karanta cikakken babi Irm 18