Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Hab 3:4-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

4. Walƙiyarsa kamar hasken rana ce,Haske yana haskakawa daga gare shi,A nan ne ya lulluɓe ikonsa.

5. Annoba tana tafe a gabansa,Cuta kuma tana bin bayansa kurkusa.

6. Ya tsaya, ya auna duniya,Ya duba, sai ya girgiza al'umman duniya.Sa'an nan madawwaman duwatsu suka farfashe,Madawwaman tuddai kuma suka zama bai ɗaya.Haka hanyoyinsa suke tun adun adun.

7. Na ga alfarwan Kushan suna cikin azaba,Labulen ƙasar Madayana suna rawar jiki.

8. Ya Ubangiji, ka hasala da koguna ne?Ko kuwa ka yi fushi da koguna?Ko kuwa ka hasala da teku ne,Sa'ad da ka hau dawakanka, kana bisa karusarka ta nasara?

9. Ka ja bakanka,Ka rantsar da sandunan horo.Ka rarratsa duniya da koguna.

Karanta cikakken babi Hab 3