Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Fit 5:11-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

11. Ku je, ku da kanku, ku nemi budu inda duk za ku iya samowa, amma daɗai, ba za a sawwaƙe muku aikinku ba.”’

12. Sai jama'a suka watsu ko'ina cikin ƙasar Masar, suna tattara budu.

13. Shugabannin aikin gandun suka matsa musu, suna cewa, “Sai ku cika aikinku na kowace rana daidai yadda kuke yi a dā lokacin da ake ba ku budu.”

14. Aka kuwa bulali manya waɗanda suke Isra'ilawa waɗanda shugabannin aikin gandu na Fir'auna suka sa a bisa Isra'ilawa, ana cewa, “Me ya sa jiya da yau ba ku cika yawan tubalin da aka ƙayyade, kamar dā ba?”

15. Manyan Isra'ilawa kuwa suka tafi suka yi kuka a gaban Fir'auna, suka ce, “Me ya sa ka yi wa bayinka haka?

16. Ba a ba mu budu, amma ana ce mana mu yi tubali. Ga shi ma, dūkan bayinka suke yi. Ai, jama'arka ne suke da laifin.”

17. Fir'auna kuwa ya ce musu, “Ku ragwaye ne ƙwarai, shi ya sa kuke cewa a bar ku ku tafi, ku miƙa wa Ubangiji hadaya.

18. Ku tafi, ku kama aiki, ba za a ba ku budu ba, duk da haka za ku cika yawan tubali da aka sa muku.”

19. Manyan Isra'ilawa suka ga lalle sun shiga uku, da yake aka ce dole su cika yawan tubali da aka yanka musu kowace rana.

20. Da suka fita daga gaban Fir'auna, sai suka sadu da Musa da Haruna, suna jiransu.

21. Suka ce wa Musa da Haruna, “Allah ya duba, ya hukunta ku, gama kun sa mun yi baƙin jini a wurin Fir'auna da barorinsa, har suka ɗauki takobi don su kashe mu.”

Karanta cikakken babi Fit 5