Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Fit 3:10-13 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. Zo, in aike ka wurin Fir'auna domin ka fito da jama'ata, wato Isra'ilawa, daga cikin Masar.”

11. Amma Musa ya ce wa Allah, “Wane ni in tafi gaban Fir'auna in fito da Isra'ilawa daga cikin Masar?”

12. Sai Allah ya ce, “Zan kasance tare da kai, wannan kuwa zai zama alama a gare ka, cewa ni ne na aike ka. Sa'ad da ka fito da jama'ar daga Masar, za ku bauta wa Allah a bisa dutsen nan.”

13. Sai Musa ya ce wa Allah, “Idan na je wurin Isra'ilawa na ce musu, ‘Allah na ubanninku ya aiko ni gare ku,’ idan sun ce mini, ‘Yaya sunansa?’ Me zan faɗa musu?”

Karanta cikakken babi Fit 3