Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Fit 22:19-31 Littafi Mai Tsarki (HAU)

19. “Duk wanda ya kwana da dabba, lalle kashe shi za a yi.

20. “Wanda ya miƙa hadaya ga wani allah, ba ga Ubangiji ba, sai a hallaka shi ɗungum.

21. “Kada ku wulakanta baƙo ko ku zalunce shi, gama dā ku baƙi ne a ƙasar Masar.

22. Kada ku ci zalun marayu da gwauraye.

23. In kun tsananta musu, ba shakka za su yi kuka gare ni, ni kuma, hakika zan ji kukansu.

24. Zan husata, in sa a kashe ku cikin yaƙi, matanku, su ma, su zama gwauraye, 'ya'yanku kuwa su zama marayu.

25. “Idan kun ranta wa jama'ata matalauta da suke tsakaninku kuɗi, ba za ku zama musu kamar masu ba da rance da ruwa ba. Kada ku nemi ruwan kuɗin daga gare su.

26. In har wani ya karɓi rigar amininsa jingina, lalle ne ya mayar masa da ita kafin faɗuwar rana.

27. Gama wannan ne kaɗai mayafinsa, da shi zai rufe huntancinsa. Da me zai rufa ya yi barci? Zan amsa masa kuwa in ya yi kuka gare ni, gama cike nake da juyayi.

28. “Kada ku saɓi Allah, kada kuma ku zagi mai mulkin jama'arku.

29. “Kada ku yi jinkirin fitar da zakar amfanin gonarku ta hatsi da ta abin matsewa.'Ya'yan farinku, maza, kuma za ku ba ni su.

30. Haka kuma za ku yi da 'ya'yan farin shanunku, da na awakinku, da na tumakinku. Ɗan farin zai yi kwana bakwai tare da uwar, amma a rana ta takwas za ku ba ni shi.

31. “Za ku zama keɓaɓɓun mutane a gare ni. Kada ku ci dabbar da naman jeji ya yayyage shi, sai ku jefa wa karnuka.”

Karanta cikakken babi Fit 22