Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Fit 19:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Isra'ilawa sun kai jejin Sina'i a farkon watan uku bayan fitowarsu daga ƙasar Masar.

2. Da suka tashi daga Refidim, suka shiga jejin Sina'i, sai suka yi zango gaban dutsen.

3. Musa kuwa ya hau bisa dutsen don ya sadu da Allah.Ubangiji ya kira shi daga kan dutsen, ya ce, “Abin da za ka faɗa wa gidan Yakubu, wato Isra'ilawa ke nan,

4. ‘Kun dai ga abin da na yi da Masarawa, da yadda na ɗauke ku kamar yadda gaggafa take ɗaukar 'yan tsakinta, na kawo ku gare ni.

5. Yanzu fa, in za ku yi biyayya da ni, ku kuma kiyaye maganata, za ku zama mutanena. Dukan duniya tawa ce, amma ku za ku zama zaɓaɓɓiyar jama'ata,

Karanta cikakken babi Fit 19