Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Fit 13:19-22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

19. Musa ya kuma ɗauki ƙasusuwan Yusufu, gama Yusufu ya riga ya rantsar da Isra'ilawa su kwashe ƙasusuwansa daga Masar sa'ad da Allah ya ziyarce su.

20. Sai suka ci gaba da tafiya daga Sukkot suka yi zango a Etam a gefen jejin.

21. Da rana Ubangiji yakan yi musu jagora da al'amudin girgije, da dare kuwa da al'amudin wuta, domin ya ba su haske domin su iya tafiya dare da rana.

22. Al'amudan nan biyu kuwa, na girgijen da na wutar, ba su daina yi wa jama'a jagora ba.

Karanta cikakken babi Fit 13