Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Fit 10:26-29 Littafi Mai Tsarki (HAU)

26. Don haka sai mu tafi da dabbobinmu, ko kofato ba za a bari a baya ba, gama daga cikinsu ne za mu ɗibi abin da za mu miƙa wa Ubangiji Allahnmu. Ba mu kuma san irin abin da za mu miƙa wa Ubangiji ba, sai mun kai can.”

27. Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir'auna har bai yarda ya sake su ba.

28. Fir'auna ma ya ce wa Musa, “Tafi, ka ba ni wuri, ka mai da hankali fa, kada in ƙara ganinka, gama ran da na sāke ganinka ran nan kā mutu.”

29. Sai Musa ya amsa ya ce, “Haka nan ne kuwa, ba zan ƙara ganin fuskarka ba.”

Karanta cikakken babi Fit 10