Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Far 27:1-4 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Lokacin da Ishaku ya tsufa, idanunsa kuma suka yi duhu har ba ya iya gani, sai ya kira Isuwa babban ɗansa, ya ce masa, “Ɗana!”Sai ya amsa, “Ga ni nan.”

2. Ishaku ya ce, “Ga shi, na tsufa, ban san ranar rasuwata ba.

3. Yanzu fa, ka ɗauki makamanka, da kwarinka da bakanka, ka tafi jeji ka farauto mini nama,

4. ka shirya mini abinci mai daɗi irin wanda nake so, ka kawo mini in ci, don in sa maka albarka kafin in rasu.”

Karanta cikakken babi Far 27