Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 39:26-29 Littafi Mai Tsarki (HAU)

26. Sa'ad da suka komo suka zauna lafiya a ƙasarsu, za su manta da abin kunyar da suka yi da dukan ha'incin da suka yi mini. Ba wanda zai ƙara firgita su, ba kuwa mai tsorata su.

27. Zan nuna wa sauran al'umma ni mai tsarki ne ta wurin komo da mutanen Isra'ila daga cikin al'ummai, da ƙasashen al'ummai magabtansu.

28. Sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji Allahnsu, domin na kore su daga ƙasarsu zuwa bautar talala cikin al'ummai, sa'an nan na sāke tattaro su zuwa cikin ƙasarsu. Daga cikinsu ba zan bar ko ɗaya a cikin al'ummai ba.

29. Ba kuma zan ƙara kawar da fuskata daga gare su ba, sa'ad da na saukar da Ruhuna a kan jama'ar Isra'ila, ni Ubangiji na faɗa.”

Karanta cikakken babi Ez 39