Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 39:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. “Kai ɗan mutum, sai ka faɗa wa Gog shugaban Rosh, da Meshek, da Tubal cewa, ‘Ni Ubangiji Allah ina gāba da kai.

2. Zan juya ka in sa ka gaba in tashi daga ƙurewar arewa, in kawo ka don ka fāɗa wa duwatsun Isra'ila.

3. Sa'an nan zan karya bakan da yake a hannun hagunka, in sa kiban da suke a hannun damanka su fāɗi.

4. Za ka fāɗi matacce a kan duwatsun Isra'ila, kai da dukan rundunanka, da jama'ar da suke tare da kai. Zan ba da gawawwakinka ga tsuntsaye da dabbobi masu cin nama.

5. Za ka mutu a filin saura, gama haka ni Ubangiji Allah na faɗa.’

Karanta cikakken babi Ez 39