Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 35:10-15 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. “Da yake ya ce al'umman nan biyu, da ƙasashen nan biyu za su zama nasa, ya mallake su, ko da yake Ubangiji yana cikinsu,

11. domin haka, ni Ubangiji Allah na ce, hakika zan saka masa gwargwadon fushinsa, da kishinsa, da ƙiyayyar da ya nuna musu. Zan sanar da kaina a gare su sa'ad da na hukunta shi.

12. Zai sani Ubangiji ne wanda ya ji dukan zarge zargen da ya yi wa duwatsun Isra'ila, da ya ce, ‘An maishe su kufai marar amfani, an ba mu su mu cinye!’

13. Na ji tsiwa da dukan surutan da ya yi mini.

14. “Ni Ubangiji Allah zan maishe shi kufai marar amfani, domin dukan duniya ta yi farin ciki.

15. Kamar yadda ya yi farin ciki saboda gādon jama'ar Isra'ila, da ya zama kufai marar amfani, haka nan zan yi da shi, wato Seyir. Zai zama kufai marar amfani, wato Dutsen Seyir da dukan Edom. Sa'an nan mutane za su sani ni ne Ubangiji!”

Karanta cikakken babi Ez 35