1. A kan rana ta fari, ga watan goma sha biyu, a shekara ta goma sha biyu, sai Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce,
2. “Ɗan mutum, ka yi makoki a kan Fir'auna, Sarkin Masar, ka ce,‘Ka aza kanka kamar zaki a cikin al'ummai,Amma kai kada ne a cikin ruwa.Ka ɓullo cikin kogunanka,Ka gurɓata ruwa da ƙafafunka,Ka ƙazantar da kogunansu.’
3. Ubangiji Allah ya ce,‘Zan jefa taruna a kanka, a babban taron mutane,Zan jawo ka cikin taruna.
4. Zan jefar da kai a tudu,A fili zan jefa ka.Zan sa tsuntsayen sararin sama su ɗira a kanka,Zan ƙosar da namomin jeji na dukan duniya da namanka.
5. Zan watsa namanka a kan duwatsu,In cika kwaruruka da gawarka.