14. Zan sa Fatros ta zama kufai,Zan kunna wa Zowan wuta,Zan kuma shara'anta No.
15. Zan kwarara hasalata a kan Felusiyum,Wato kagarar Masar,Zan datse jama'ar No.
16. Zan kunna wa Masar wuta.Felusiyum za ta sha azaba mai tsanani,No kuwa za a tayar mata da hankali,Za a rurrushe garukanta.Za a tasar wa Memfis dukan yini.
17. Samarin Awen da na Fi-besetZa a kashe su da takobi,Matan kuma za su tafi bauta.
18. A Tafanes rana za ta yi duhu,Sa'ad da na karya mulkin ƙasar Masar,Ƙarfinta da take fariya da shi zai ƙare,Za a rufe ta da gizagizai.'Ya'yanta mata kuwa za a kai su bauta.
19. Ta haka zan hukunta Masar,Sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji.”