Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 23:30-47 Littafi Mai Tsarki (HAU)

30. Lalatarki da karuwancinki su suka jawo miki wannan, gama kin yi karuwanci da sauran al'umma kika ƙazantar da kanki da gumakansu.

31. Kin bi halin 'yar'uwarki, domin haka zan hukunta ki kamar yadda na hukunta ta.’ ”

32. Ubangiji Allah ya ce,“Za ki sha babban hukuncin da 'yar'uwarki ta sha,Za a yi miki dariya da ba'a,Gama hukuncin yana da tsanani.

33. Za ki sha wahala da baƙin ciki,Hukunci na bantsoro da lalacewa,Shi ne irin hukuncin da aka yi wa 'yarki Samariya.

34. Ƙoƙon da kika sha hukunci daga ciki, za ki lashe shi,Ki tattaune sakainunsa,Ki tsattsage nononki,Ni Ubangiji Allah na faɗa.”

35. Ubangiji ya ce, “Da yake kin manta da ni, kin ba ni baya. Don haka ki ɗauki hakkin lalatarki da karuwancinki.”

36. Sai Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, ko ka shara'anta wa Ohola da Oholiba? To, sai ka faɗa musu mugayen ayyukansu.

37. Gama sun yi zina da kisankai, sun bauta wa gumakansu, har ma sun miƙa musu 'ya'yansu maza da suka haifa mini, su zama abincinsu.

38. Ga kuma abin da suka yi mini, sun ƙazantar da Haikalina a ranar, sun kuma ɓata ranar Asabar ɗina.

39. Gama a ranar da suka kashe 'ya'yansu, suka miƙa su hadaya ga gumakansu, sai suka shiga Haikalina suka ƙazantar da shi. Abin da suka yi ke nan cikin Haidalina.

40. “Kun aiki manzo wurin mutanen da suke nesa su kuwa suka zo. Saboda su kun yi wanka, kun sa kwalli, kun ci ado.

41. Kun zauna a gado mai daraja, da tebur a shirye a gabansa. A kansa kuka ajiye turarena da maina.

42. A wurinta akwai hayaniyar taron mutane marasa kula, sai kuma aka kawo mutane irinsu, mashaya daga jeji. Suka sa mundaye a hannuwan matan, suka kuma sa kambi masu kyau a kawunansu.

43. Sai na yi magana a kanta, ita wadda ta ƙare ƙarfinta da yin zina, yanzu za su yi zina da ita da ta zama haka?

44. Suka shiga wurinta kamar yadda akan shiga wurin karuwa. Haka kuwa suka shiga wurin Ohola da Oholiba don su yi zina da su.

45. Amma adalai za su yanka musu hukunci irin wanda akan yi wa mata mazinata, da mata masu kisankai, gama su mazinata ne masu kisankai.

46. “Gama ni Ubangiji Allah na ce, a kawo rundunar soja ta yi yaƙi da su, don su firgita su, su washe su.

47. Rundunar za ta jajjefe su da duwatsu, ta sassare su da takuba. Za ta kuma kashe 'ya'yansu mata da maza, ta ƙone gidajensu.

Karanta cikakken babi Ez 23