Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Ez 23:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Sai Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce,

2. “Ɗan mutum, akwai waɗansu mata biyu, uwarsu ɗaya.

3. Sun yi karuwanci a Masar, a lokacin 'yan matancinsu, aka rungumi mamansu da ƙirjinsu.

4. Sunan babbar Ohola, sunan ƙanwar kuwa Oholiba. Sun zama nawa, sun haifi 'ya'ya mata da maza. A kan sunayensu kuwa Ohola ita ce Samariya, Oholiba kuwa ita ce Urushalima.

5. Ohola ta yi karuwanci sa'ad da take zamana. Ta yi ta kai da kawowa a tsakanin kwartayenta, Assuriyawa,

Karanta cikakken babi Ez 23